Saturday, 8 July 2017

ADDU'AR SALLAR ISTIHARA (neman zabi ga Allah)




Addu'ar Sallar Istihara (Neman Zabin Allah Idan Mutum Zai AikaTa Wani Abu).

Jabir Ibn Abdullah, Allah ya yarda da shi da mahaifinsa, ya ce; Manzon Allah (SAW), tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya kasance yana koya mana yin istihara (neman zabin Allah) a Cikin dukkan al'amura kamar yadda yake koya mana sura daga Cikin Alkur'ani, yakan ce, "Idan dayanku ya yi niyyar yin wani al'amari to ya yi sallah raka'a biyu ba ta farilla ba, sannan ya ce;
اَللَّهُمَّ إِنِّي أَسْتَخِيرُكَ بِعِلْمِكَ، وَأسْتَقْدِرُكَ بِقُدْرَتِكَ، وَأَسْألُكَ مِنْ فَضْلِكَ الْعَظِيم، فَإِنَّكَ تَقْدِرُ وَلا أَقْدِر، وَتَعْلَمُ وَلا أَعْلَم، وَأَنْتَ عَلاّمُ الغُيوبِ، اللّهُمَّ إِنْ كُنْتَ تَعْلَمُ أَنَّ هَذَا اْلأَمْرَ- وَيُسَمِّي حَاجَتَهُ - خَيْرٌ لِي فِي دِينِي وَمَعَاشِي وَعَاقِبَةِ أَمْرِي، عَاجِلِهِ وَأَجِلِهِ فَاقْدُرْهُ لِي وَيَسِّرْهُ لِي ثُمَّ بَارِكْ لِي فِيهِ، وَإِنْ كُنْتَ تَعْلَمُ أَنَّ هَذَا اْلأَمْرَ شَرٌ لِي فِي دِينِي وَمَعَاشِي وَعَاقِبَةِ أَمْرِي، فَاصْرِفْهُ وَاصْرِفْنِي عَنْهُ وَاقْدُرْ لِي الْخَيْرَ  حَيْثُ كَانَ ثُمَّ أَرْضِنِي بِهِ.
Allahumma innee astakheeruka bi'ilmik, wa-astaqdiruka biqudratik, wa-as-aluka min fadlikal-'azeem, fa-innaka taqdiru wala aqdir, wata'lamu wala a'lam ,wa-anta 'allamul ghuyoob, allahumma in kunta ta'lamu anna hazal-amr (say your need) khayrun lee fee deenee wama'ashee wa'akibati amree fakqurhu lee, wayassirhu lee, thumma barik lee feeh, wa-in kunta ta'lamu anna hazal-amr sharrun lee fee deenee wama'ashee wa'aqibati amree fasrifhu 'annee wasrifnee 'anh, waqdur liyal-khayra haythu kan, thumma ardinee bihi.

Ya Allah! Ina neman zabinka domin iliminka, kuma ina neman Ka ba ni iko domin Ikonka, kuma ina rokonka daga falalarka Mai girma; domin Kai ne mai iko ni kuwa ba ni iko, kuma Kai ne Masani, ni kuwa ban sani ba, kuma Kai ne masanin abubuwan fake. Ya Allah! Idan ka san cewa wannan al'amari sai ya ambaci bukata tasa alheri ne gare ni a cikin addinina, da rayuwata, da kuma karshen al'amarina a wata rayuwar; da magaggaucin ala'marina da majinkircinsa Ka kaddara mini shi, kuma Ka saukake mini shi, sannan Ka albarkance ni a cikin sa. Kuma idan Ka san wannan al'amari sharri ne gare ni a cikin addinina, da rayuwata da karshen al'amarina a wata ruwayar; da magaggaucin al'amarina da majinkircinsa – Ka kawar da shi daga gare ni, kuma Ka  kawar da ni daga gare shi, kuma Ka kaddara mini alherin a duk inda yake, kuma Ka sanya ni in yarda da shi".

Duk wanda ya nemi zabin mahalicci, kuma ya yi shawara da talikai muminai, kuma ya yi azama a Cikin lamarinsa, to ba zai yi nadama ba, domin Allah madaukakin sarki Ya ce;
(وَشَاوِرْهُمْ فِي اْلأَمْرِ فَإِذَا عَزَمْتَ فَتَوَكَّلْ عَلَى اللهِ)
(Washawirhum Fiyl Amri Fa'iza Azamta Fatawakkal Alallahi).

"Kuma ka shawarce su cikin lamarinka, idan kuma ka kuduri aniya, to ka dogara ga Allah".

ZIKIRI BAYAN ANYI SALLAMA DAGA SALLAH


Zikiri Bayan An Yi Sallama Daga Sallah

أَسْـتَغْفِرُ الله (ثَلاثاً) اللّهُمَّ أَنْتَ السَّلامُ، وَمِنْكَ السَّلامُ، تَبارَكْتَ يَا ذَا الْجَلاَلِ وَالإِكْرَامِ.
Astaghfirul-lah (3) Allahumma antas-salam waminkas-salam, tabarakta ya zal-jalali wal-ikram.

Ina neman tsarin Allah (sau uku).
Ya Allah! Kai ne Aminci, kuma daga gare Ka Aminci ya ke, alherinKa ya yawaita; ya ma'abocin girma da alheri.


لاَ إلَهَ إلاَّ اللَّهُ وحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ، لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ، وَهُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ، اَللَّهُمَّ لاَ مَانِعَ لِمَا أَعْطَيْتَ، وَلاَ مُعْطِيَ لِمَا مَنَعْتَ، وَلاَ يَنْفَعُ ذَا الْجَدِّ مِنْكَ الْجَدُّ .
La ilaha illal-lahu wahdahu la shareeka lah, lahul-mulku walahul-hamd, wahuwa ala kulli shayin qadeer, allahumma la mani'a lima a'tayta, wala mu'tiya lima mana'ata, wala yanfa'u thal-jaddi minkal-jad.

Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai, babu abokin tarayya a gare Shi. Mulki na Sa ne (Shi kadai) kuma yabo na Sa ne (Shi kadai), kuma Shi ne Mai iko kan komai. Ya Allah! Babu mai hana abin da Ka bayar kuma babu mai bayar da abin da Ka hana, kuma wadda ba ta tsirar da mai wadata daga gare Ka.

لاَ إلَهَ إلاَّ اللَّهُ, وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ، لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ، وَهُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ، لاَ حَوْلَ وَلاَ قُوَّةَ إِلاَّ بِاللهِ، لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللَّهُ، وَلاَ نَعْبُدُ إِلاَّ إِيَّاهُ, لَهُ النِّعْمَةُ وَلَهُ الفَضْلُ وَلَهُ الثَّنَاءُ الْحَسَنُ، لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللَّهُ مُخْلِصِينَ لَهُ الدِّينَ وَلَوْ كَرِهَ الْكَافِرُونَ.
La ilaha illal-lah, wahdahu la shareeka lah, lahul-mulku walahul-hamd, wahuwa ala kulli shayin kadeer. la hawla wala quwwata illa billah, la ilaha illal-lah, wala na'abudu illa iyyah, lahun-ni'matu walahul-fadl walahuth-thana-ol- hasan, la ilaha illal-lah mukhliseena lahud-deen walaw karihal-kafiroon.

Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai, babu abokin tarayya a gare Shi. Mulki na Sa ne (Shi kadai), kuma yabo na Sa ne (Shi kadai), kuma Shi ne Mai iko a kan komai. Kuma babu dabara babu karfi sai da Allah. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah; kuma ba ma bautawa kowa sai Shi. Ni'ima tasa ce, kuma falala tasa ce, kuma kyakkyawan yabo nasa ne. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, muna masu tsarkake bauta (daga shirka) a gare Shi, ko da kafirai sun ki.



سُبْحَانَ اللهِ، وَالْحَمْدُ ِللهِ، وَاللهُ أكْبَرْ. (ثلاثاً وثلاثين) لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللّهُ وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ، لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ، وَهُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ.
Subhanal-lah walhamdu lillah, wallahu akbar (33). La ilaha illal-lahu wahdahu la shareeka lah, lahul-mulku walahul-hamdu, wahuwa 'ala kulli shay'in qadir

Tsarki ya tabbata ga Allah, kuma godiya ta tabbata ga Allah, kuma Allah Shi ne mafi girma. (Sau 33). Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, (Shi kadai), kuma Shi ne Mai iko kan koma.

 Ana karanta wadannan surorin (kowace daga ciki har izuwa karshenta) bayan kowace sallah; amma bayan sallar Asuba da Magariba ana karanta su sau uku.


بسم الله الرحمن الرحيم{ قُلْ هُوَ اللَّهُ أَحَدٌ*اللَّهُ الصَّمَدُ*لَمْ يَلِدْ وَلَمْ يُولَدْ *وَلَمْ يَكُن لَّهُ كُفُواً أَحَدٌ}

Bismi l-lahi r-rahmani r-rahimi.
Kul huwa l-lahu ahad, Allahu s-samad, Lam yalid wa lam yulad, wa lam yakun lahu kufu'an ahad.
{قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ الْفَلَقِ * مِن شَرِّ مَا خَلَقَ *وَمِن شَرِّ غَاسِقٍ إِذَا وَقَبَ * وَمِن شَرِّ النَّفَّاثَاتِ فِي الْعُقَدِ * وَمِن شَرِّ حَاسِدٍ إِذَا حَسَدَ }
Bismi l-lahi r-rahmani r-rahimi.
Kul a'udhu bi-rabbi-l-falaq, min sharri ma khalaq, wa min sharri ghasikin idha waqab, wa min sharrin n-naffathati fi-l-'uqad, wa min sharri hasidin idha hasad.

بسم الله الرحمن الرحيم {قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ النَّاسِ * مَلِكِ النَّاسِ * إِلَهِ النَّاسِ *مِن شَرِّ الْوَسْوَاسِ الْخَنَّاسِ * الَّذِي يُوَسْوِسُ فِي صُدُورِ النَّاسِ * مِنَ الْجِنَّةِ وَالنَّاسِ}

Bismi l-lahi r-rahmani r-rahimi.
Kul a'udhu bi-rabbi n-nas, maliki n-nas, ilahi n-nas, min sharri-l-waswasi-l-khannas, al-ladhi yuwaswisu fi suduri n-nas, mina-l-jannati wa n-nas.

Bayan kowace sallah sannan a k

Friday, 7 July 2017

TAHIYYA DA SALATI GA ANNABI (SAW)


Tahiyya

اَلتَّحِيَّاتُ ِللهِ وَالصَّلَوَاتُ والطَّيِّبَاتُ، اَلسَّلاَمُ عَلَيْكَ  أَيُّهَا النَّبِيُّ  وَرَحْمَةُ اللهِ وَبَرَكَاتُهُ، اَلسَّلاَمُ عَلَيْنَا وَعَلَى عِبَادِكَ الصَّالِحِينَ. أَشْهَدُ أَنْ لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللهُ، وَأَشْهَدُ أَنَّ مُحَمَّداً عَبْدُهُ وَرَسُولُه .
Attahiyyatu lillahi wassalawatu wattayyibat, assalamu AAalayka ayyuhan-nabiyyu warahmatul-lahi wabarakatuh, assalamu 'alayna wa'ala ibadil-lahis-saliheen. Ash-hadu an la ilaha illal-lah, wa-ashhadu anna Muhammadan 'abduhu warasooluh.

Dukkan nau'in ban girma ya tabbata ga Allah, da kuma salloli da kyawawan kalmomi. Aminci ya tabbata gare ka ya Annabi, da rahamar Allah da albarkatunsa. Aminci ya tabbata gare mu, da kuma ga bayin Allah salihai ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah. Kuma ina shaidawa cewa Muhammad bawansa ne kuma Manzonsa ne.



Salati Ga Annabi, Tsira da Amincin Allah Su Tabbata A Gare shi, bayan Tahiya;

اَللّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ، وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اَللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ، وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارِكْتَ عَلَى إبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ. 
Allahumma salli 'ala Muhammad, wa-'ala ali Muhammad, kama sallayta 'ala Ibraheema wa-'ala ali Ibraheem, innaka Hameedun Majeed, allahumma barik 'ala  Muhammad, wa-'ala ali Muhammad, kama barakta 'ala Ibraheema wa-'ala ali Ibraheem, innaka Hameedun Majeed.


Ya Allah! Ka yi salati ga Muhammadu, da alayen Muhammadu, kamar yadda kayi salati ga Ibrahimu da alayen Ibrahim, lallai kai abin godewa ne, mai girma. Ya Allah! Ka yi albarka ga Muhammadu, da alayen Muhammadu, kamar yadda ka yi albarka ga Ibrahimu, da alayen Ibrahimu, lallai kai abon godewa ne, mai girma.

اَللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ  وَعَلَى أَزْوَاجِهِ وَذُرِّيَّتِهِ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى آلِ إبْرَاهِيمَ. وَبَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى أَزْوَاجِهِ وَذُرِّيَّتِهِ، كَمَا بَارِكْتَ عَلَى آلِ إبْرَاهِيمَ. إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ.
Allahumma salli AAala Muhammad wa-'ala azwajihi wathurriyyatihi kama sallayta 'ala ali Ibraheem, wabarik 'ala Muhammad, wa-'ala azwajihi wathurriyyatih, kama barakta 'ala ali Ibraheem. innaka Hameedun Majeed.

Ya Allah! Ka yi salati ga Muhammadu, da kuma ga matansa da zuriyarsa, kamar yadda ka yi salati ga alayen Ibrahim. Kuma ka yi albarka ga Muhammadu, da kuma ga matansa da zuriyarsa, kamar yadda ka yi albarka ga alayen Ibrahim. Lallai kai abin godewa ne, mai girma.


اَللّهُمَّ إِنِّي أَعُوذُ بِكَ مِنْ عَذَابِ القَبْرِ، وَمِنْ عَذَابِ جَهَنَّمَ، وَمِنْ فِتْنَةِ الْمَحْيَا وَالْمَمَاتِ، وَمِنْ شَرِّ فِتْنَةِ  الْمَسِيحِ الدَّجَّالِ.
Allahumma innee a'u'zu bika min 'athabil-kabr, wamin 'azabi jahannam, wamin fitnatil-mahya walmamat, wamin shari fitnatil-maseehid-dajjal.

Ya Allah ina neman tsari da Kai daga azabar kabari, da azabar Jahannama, da fitinar rayuwa da ta mutuwa, da sharrin fitinar Dujal shafaffe.


اللّهُـمَّ إِنِّـي أَعـوذُ بِكَ مِـنْ عَذابِ القَـبْرِ، وَأَعـوذُ بِكَ مِـنْ فِتْـنَةِ  المَسيحِ الدَّجّـالِ، وَأَعـوذُ بِكَ مِـنْ فِتْـنَةِ  المَحْـيا وَالْمَمَـاتِ. اللّهُـمَّ إِنِّـي أَعـوذُ بِكَ مِنَ المَأْثَـمِ وَالمَغْـرَم .
Allahumma innee a'u'zu bika min azabil-kabr, wa-a'u'zu bika min fitnatil-maseehid-dajjal, wa-a'u'zu bika min fitnatil-mahya walmamat. Allahumma innee a'u'zu bika minal-ma'thami walmaghram.

Ya Allah! Ina neman tsarinka daga azabar kabari, kuma ina neman tsarinka daga fitinar Dujal shafaffe, kuma ina neman tsarinKa daga fitinar rayuwa da ta mutuwa. Ya Allah ina neman tsarinka daga laifi da bashi.


اَللَّهُمَّ إِنِّي ظَلَمْتُ نَفْسِي ظُلْمًا كَثِيراً وَلاَ يَغْفِرُ الذُّنُوبَ إِلاَّ أَنْتَ، فَاغْفِرْلِي مَغْفِرَةً مِنْ عِنْدِكَ وَارْحَمْنِي، إِنَّكَ أَنْتَ الغَفُورُ الرَّحِيم .
Allahumma innee zalamtu nafsee zulman katheeran wala yaghfiruz-zunooba illa ant, faghfir lee maghfiratan min 'indika warhamnee, innaka antal-Ghafoorur-Raheem.


Ya Allah! Hakika ni na zalunci kai na, zalunci mai yawa, kuma babu mai gafarta zunubai sai Kai. Saboda haka Ka gafarta mini, gafara daga gare Ka, kuma Ka ji kai na, lallai Kai ne mai yawan gafara, mai yawan jin kai.


اَللَّهُمَّ اغْفِرْلِي مَاقَدَّمْتُ وَمَا أَخَّرْتُ، وَمَا أَسْرَرْتُ وَمَا أَعْلَنْتُ، وَمَا أَسْرَفْتُ، وَمَا أَنْتَ أَعْلَمُ بِهِ مِنِّي. أَنْتَ الْمُقَدِّمُ، وَأَنْتَ الْمُؤَخِّرُ لاَ إِلَهَ إِلاَّ أَنْتَ.
Allahummagh-fir lee ma kaddamtu,  wama akhkhart, wama asrartu wama a'alant, wama asraftt, wama anta a'alamu bihi minnee, antal-mukaddimu wa-antal-mu-akhkhiru la ilaha illa anta.

Ya Allah ka gafarta mini abin da ya wuce da abin da zai zo, da abin da na boye da abin da na bayyana, da kuma abin da Kai ne Ka fi fi ni saninsa. Kai ne Mai gabatarwa, kuma Kai ne Mai jinkirtawa; babu abin bautawa da gaskiya sai Kai.

اَللَّهُمَّ أَعِنِّي عَلَى ذِكْرِكَ وَشُكْرِك، وَحُسْنِ عِبَادَتِكَ.
Allahumma a'innee 'al

ADDU'AR SUJADAH DA TSAKANIN TA FARKO DA TA BIYU


Addu'ar Sujjada

سُبْحَانَ رَبِّيَ الأَعْلَى . (ثلاثَ مَرَّاتٍ)
Subhana rabbiyal-a'la. (3)

Tsarki ya tabbata ga Ubangijina mafi daukaka.


سُبْحَانَكَ اَللَّهُمَّ رَبَّنَا وَبِحَمْدِكَ، اَللَّهُمَّ اغْفِرْلِي.
Subhanakal-lahumma rabbana wabihamdik, allahummagh- fir lee.

Tsarki ya tabbata gare Ka, Ya Allah! Ya Ubangijinmu! Tare da godiya gare Ka. Ya Allah! Ka gafarta mini.


سُبُّوحٌ قُدُّوس، رَبُّ الملائِكَةِ وَالرُّوحُ .
Subbohoon kuddos, rabbul-mala-ikati warrooh.

(Ubangiji) abin tsarkakewa, mai kubuta daga dukkan abin da bai kamace shi ba, Ubangijin Mala'iku da Jibrilu.


اَللَّهُمَّ لَكَ سَجَدْتُ وَبِكَ آمَنْتُ، وَلَكَ أَسْلَمْتُ، سَجَدَ وَجْهِي ِللَّذِي خَلَقَـهُ وَصَوَّرَهُ وَشَقَّ سَمْعَهُ وَبَصَرَهُ، تَبَارَكَ اللهُ أَحْسَـنُ الْخَالِقِين.
Allahumma laka sajadt, wabika amant, walaka aslamt, sajada wajhee lillathee khalaqahu wasawwarahu washaqqa sam'ahu wabasarahu, tabarakal-lahu ahsanul-khaliqeen.


Ya Allah! Gare ka na yi sujada, kuma da Kai na yi imani, kuma gare Ka na mika wuya. Fuskata ta yi sujada ga wanda ya halicce ta, kuma ya yi mata surarta, kuma ya tsaga ji da gani a gare ta. Allah mafi gwanintar masu halitta, ya girma, kuma alherinsa ya yawaita.


سُبْحَانَ ذِي الْجَبَرُوتِ، وَالْمَلَكُوتِ، وَالْكِبْرِيَاءُ، وَالْعَظَمَة.
Subhana thil-jabaroot, walmalakoot, walkibriya'i, wal'azamah.

Tsarki ya tabbata ga (Allah) mai dole, da mulki, da kasaitar daukaka da girma.


اَللّهُمَّ اغْفِرْلِي ذَنْبِي كُلَّهُ، دِقَّهُ وَجِلَّهُ، وَأَوَّلَـهُ وَآخِـرَهُ وَعَلانِيَّتَهُ وَسِرَّه .
Allahummagh-fir lee zanbee kullah, dikkahu wajillah, wa-awwalahu wa-akhirah, wa- 'alaniyyatahu wa-sirrah.


Ya Allah! Ka gafarta mini zunubaina dukkaninsu, kananansu da manyansu, na farkonsu da na karshensu, bayyanannunsu da boyayyunsu.


اَللَّهُمَّ إِنِّي أَعُوذُ بِرِضَاكَ مِنْ  سَخَطِكَ، وَبِمَعَافَاتِكَ مِنْ عُقُوبَتِكَ، وَأَعُوذُ بِكَ مِنْكَ، لاَ أُحْصِي ثَنَاءً عَلَيْكَ، أَنْتَ كَمَا أَثْنَيْتَ عَلَى نَفْسِكَ.
Allahumma innee a'uzu biridaka min sakhatik, wa-bimu'afatika min 'ukubatik, wa-a'uzu bika mink, la uhsee thana-an 'alayk, anta kama athnayta 'ala nafsik.

Ya Allah ina neman tsari da yardarka daga fushinka, da kuma rangwamanka daga ukubarka, kuma ina neman tsari da kai daga gare Ka. Ban isa na tuke ga yabo mai cancanta gare ka ba; kai dai kamar yadda Ka yabi kanKa ne.





Addu'ar Sujadar Tilawar Alkur'ani
سَجَدَ وَجْهِي ِللَّذِي خَلَقَهُ وَصَوَّرَهُ وَشَقَّ سَمْعَهُ وَبَصَـَهُ بِحَوْلِهِ وَقُوَّتِهِ تَبـارَكَ اللهُ أَحْسَـنُ الخـالِقيـن.
Sajada wajhee lillathee khalaqahu washakka sam’ahu wabasarahu bihawlihi waquwwatih  {tabaraka Allahu ahsanu alkhaliqeen}.

Fuskata ta yi sujada ga wanda ya halicce ta, kuma ya tsaga ji da gani a gare ta, da iyawarsa da kuma karfinsa, Allah mafi gwanintar masu halitta, Ya girma, kuma alherinsa ya yawaita.


اَللّهُمَّ اكْتُبْ لِي بِهَا عِنْدَكَ أَجْراً، وَضَعْ عَنِّي بِهَا وِزْراً، وَاجْعَلَهَا لِي عِنْدَكَ ذُخْراً، وَتَقَبَّلَهَا مِنِّي كَمَا تَقَبَّلْتَهَا مِنْ عَبْدِكَ دَاوُدَ.
Allahummak-tub lee biha  AAindaka ajra, wada  'annee biha wizra, waj'alha lee 'indaka zukhra, watakabbalha minnee kama takabbaltaha min 'abdika Dawood.

Ya Allah! Ka rubuta mini lada saboda ita (sujadar), ka kankare mini zunubi saboda ita, ka sanya ta ta zamo taskar arziki gare ni a wajen ka, kuma ka karbe ta daga gare ni kamar yadda ka karbe ta daga bawanka Dawuda.


ADDU'AR RUKU'U DA DAGOWA DAGA RUKU'U


Addu'ar Ruku'u

سُبْـحانَ رَبِّـيَ الْعَظـيم . (ثلاثَ مَرَّاتٍ)
 Subhana rabbiyal-a'zeem (3)

Tsarki ya tabbata ga Ubangijin mai girma (Sau uku).


سُبْحانَكَ اللّهُمَّ رَبَّنَا وَبِحَمْدِك، َاللَّّهُمَّ اغْفِرْ لِي.
Subhanakal-lahumma rabbana wabihamdik, allahummagh-fir lee

Tsarki ya tabbata gare Ka, ya Allah! Ya Ubangijinmu, tare da godiya gare Ka. Ya Allah! Ka gafarta mini.


سُبُّوحٌ قُـدُّوسٌ، رَبُّ الْمَلاَئِكَةِ وَالرُّوحُ .
Subboohun kuddoos, rabbul-mala-ikati warrooh.

(Ubangiji) abin tsarkakewa, mai kubuta daga dukkan abin da bai kamace shi ba, Ubangijin Mala'iku da Jibrilu.


اَللَّهُمَّ لَكَ رَكَعْتُ وَبِكَ آمَنْتُ، ولَكَ أَسْلَـمْتُ، خَشَعَ لَكَ سَمْعِي، وَبَصَرِي، وَمُخِّي، وَعَظْمِي، وَعَصَبِي، وَمَا اسْتَقَـلَّ بِهِ قَدَمِي.
Allahumma laka raka'atu, wabika amantu, walaka aslamtu, khasha'a laka sam'ee, wabasaree, wamukhkhee, wa'azmee, wa'asabee, wamas-takalla bihi kadamee.

Ya Allah! Gare ka na yi ruku'u, kuma da Kai na yi imani, kuma gare ka na mika wuya. Jina ya yi kaskanci gare Ka, haka ma ganina da bargona, da kashina, da jijiyata, da kuma abin da kafata ke dauke da shi.
سُبْـحَانَ ذِي الْجَبَرُوتِ، والمَلَكُوتِ، وَالْكِبْرِيَاءُ، وَالْعَظَـمَة.
Subhana thil-jabaroot, walmalakoot, walkibriya, wal'azamah.

Tsarki ya tabbata ga (Allah) Mai dole, da mulki, da kasaitar daukaka, da girma.




Addu'ar Dagowa daga Ruku'u

سَمِعَ اللهُ لِمَنْ حَمِدَهُ.
Sami'al-lahu liman hamidah

Allah Ya ji wanda ya gode masa.


رَبَّنـا وَلَكَ الحَمْـدُ حَمْداً كَثِيراً طَيِّـباً مُـبَارَكاً فِيهِ .
Rabbana walakal-hamdu hamdan katheeran tayyiban mubarakan feeh.

Ya Ubangijinmu! Dukkan yabo ya tabbata gare Ka, yabo mai yawa, kyakkyawa, kuma abin sawa albarka a cikinsa.


مِلْءَ السَّمَوَاتِ وَمِلْءَ الأَرْضِ، وَمَا بَيْنَهُمَا، وَمِلْءَ مَا شِئْتَ مِنْ شَيءٍ بَعْدُ. أَهْلَ الثَّنَاءِ وَالْمَجْدِ، أََحَقُّ مَا قَالَ العَبْدُ، وَكُلُّنَا لَكَ عَبْدُ. اَللَّهُمَّ لاَ مَانِعَ لِمَا أَعْطَـيْتُ، وَلاَ مُعْطِيَ لِمَا مَنَعْتَ، وَلاَ يَنْفَعُ ذَا الْجَدِّ مِنْكَ الْجَدُّ. 
Mil-as-samawati wamil-al-ard, wama baynahuma, wamil'a ma shi'ta min shay-in ba'd, ahlath-thana-i walmajd, ahakku ma kalal-'abd, wakulluna laka 'abd. Allahumma la mani'a lima a'tayta, wala mu'tiya lima mana'ta, wala yanfa'u zal-jaddi minkal-jaddu.

Ya Ubangiji! Dukkan yabo ya tabbata gare Ka, (yabo) mai Cika sammai da kassai da abin da ke tsakaninsu, mai cika duk wani abu da Ka so bayan haka. Ya wanda ya cancanci yabo da daukaka. (wannan yabo) shi ne mafi cancantar abin da bawa ya fada, kuma dukkanninmu bayi ne gare Ka. Ya Allah! Babu mai hana abin da Ka bayar, kuma babu mai byar da abin da Ka hana, kuma wadata ba ta tsirar da mai wadata daga gare Ka.


ADDU'AH YAYIN KIRAN SALLAH DA BUDE SALLAH


Addu’a yayin kiran Sallah :
Wanda ya ji kiran sallah zai fadi dukkan abin da ladanin yake fadi, sai dai idan yace;
حَيَّ عَلَى الصَّلاَةِ، حَيَّ عَلَى الْفَلاَحِ.
Hayya Alas Salah, Hayya Alal Falah.
Ku taho ga Sallah, ku taho ga babban rabo.

Maimakon haka sai shi ya ce:
لا حَـوْلَ وَلا قُـوَّةَ إِلاّ بِالله.
La hawla wala kuwwata illa billah.

Babu daraba, babu karfi sai da Allah.

وَأَنا أَشْـهَدُ أَنْ لاَ إِلَـهَ إِلاّ اللهُ وَحْـدَهُ لاَ شَـريكَ لَـهُ، وَأَنَّ محَمّـداً عَبْـدُهُ وَرَسُـولُهُ ، رَضِيـتُ بِاللهِ رَبَّاً ، وَبِمُحَمَّـدٍ رَسُـولاً وَبِالإِسْلامِ دِينًا .
Wa-ana ashhadu an la ilaha illal-lahu wahdahu la shareeka lah, wa-anna Muhammadan AAabduhu warasooluh, radeetu billahi rabban wabimuhammadin rasoolan wabil-islami deena.

Ni ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai, babu abokin tarayya a gare Shi. Kuma Allah shi ne Ubangiji, kuma Muhammadu shi ne Manzo, kuma Musulunci shi ne addini.


Bayan ya gama amsa kiran sallar, sai ya yi salati ga Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.

Sannan ya ce:
اللّهُـمَّ رَبَّ هَذِهِ الدّعْـوَةِ التّـامَّةِ وَالصّلاةِ القَـائِمَة آتِ محَـمَّداً الوَسيـلةَ وَالْفَضـيلَة وَابْعَـثْهُ مَقـامًـا مَحْـمُوداً الَّذِي وَعَـدْتَهُ إِنَّـكَ لا تُـخْلِفُ الْمِيـعَادَ.
 Allahumma rabba hathihid-da'watit-tammah, wassalatil-ka-imah ati Muhammadan alwaseelata wal-fadeelah, waba'ath-hu makaman mahmoodan allazee wa'adtahu, innaka la tukhliful-mee'ad.

Ya Allah! Ubangijin wannan kira kammalalle, da wannan sallar da za a tsayar da ita. Ka ba wa Muhammadu wasila (matsayin kusanci a cikin Aljanna), da matsayin fifiko, kuma ka tashe mu a matsayi abin godewa, wannan wanda Ka yi masa alkawarinsa. Lallai kai ba ka saba alkawari.


Sannan ya yiwa kansa addu'a tsakanin kiran sallah da tayar da ikama, domin addu'a a wannan lokaci ba a kin karbarta.



Addu'ar Bude Sallah (watau Bayan An yi Kabbarar Harama)

اَللَّهُـمَّ باعِـدْ بَيـنِي وَبَيْنَ خَطـايايَ كَما باعَدْتَ بَيْنَ المَشْرِقِ وَالمَغْرِبْ ، اَللَّهُـمَّ نَقِّنِـي مِنْ خَطايايَ كَمـا يُـنَقَّى الثَّـوْبُ الأَبْيَضُ مِنَ الدَّنَسْ ، اَللَّهُـمَّ اغْسِلْنِـي مِنْ خَطَايَـايَ بِالثَّلـجِ وَالمـاءِ وَالْبَرَدْ .
 Allahumma ba'id baynee wabayna khatayaya kama ba'adta baynal-mashriki walmaghrib, allahumma nakkinee min khatayaya kama yunakkath-thawbul-abyadu minad-danas, allahummagh-silnee min khatayaya biththalji walma'i walbarad.

Ya Allah! Ka nisanta tsakanina da laifuffukana kamar yadda Ka nisanta tsakanin gabas da yamma; Ya Allah! Ka tsarkake ni daga laifuffukana kamar yadda ake tsarkake farar tufa daga dauda, Ya Allah! Ka wanke ni daga laifuffukana da kankara da ruwa da raba.


سُبْـحانَكَ اللّهُـمَّ وَبِحَمْـدِكَ وَتَبارَكَ اسْمُـكَ وَتَعَـالَى جَـدُّكَ وَلا إِلهَ غَيْرُكَ.
Subhanakal-lahumma wabihamdika watabarakas-muka wata'ala jadduka wala ilaha ghayruk.

Tsarki ya tabbata gareKa, Ya Allah, tare da yabo gareka; Albarkatun sunanka sun yawaita; mulkinka da girmanka sun daukaka; babu abin bautawa da gaskiya ba Kai ba.

 
وَجَّهـْتُ وَجْهِـيَ لِلَّذِي فَطَرَ السَّمـَوَاتِ وَالأَرْضَ حَنِـيفَاً وَمَـا أَنَا مِنَ المشْرِكِينَ، إِنَّ صَلاَتِـي، وَنُسُكِي، وَمَحْـيَايَ ، وَمَمَاتِـي ِللهِ رَبِّ العالَمِينَ، لاَ شَرِيـكَ لَهُ وَبِذَلِكَ أُمِرْتُ وَأَنَا مِنَ الْمُسْلِـمِينَ. اَللَّهُـمَّ أَنْتَ المَلِكُ لاَ إِلهَ إِلاَّ أَنْتَ ،أَنْتَ رَبِّـي وَأَنَـا عَبْـدُكَ ، ظَلَمْـتُ نَفْسِـي وَاعْـتَرَفْتُ بِذَنْبِـي فَاغْفِرْ لِي ذُنُوبِي جَمِيعاً إِنَّـهُ لاَ يَغْـفِرُ الذُّنـُوبَ إلاّ أَنْتَ .وَاهْدِنـِي لأَحْسَنِ الأَخْلاقِ لاَ يَهْـدِي لأَحْسَـنِهَا إِلاَّ أَنْـتَ، وَاصْـرِفْ عَـنِّي سَيِّئَهَـا، لاَ يَصْرِفُ عَـنِْي سَيِّئَهَـا إِلاَّ أَنْـتَ، لَبَّـيْكَ وَسَعْـدَيْكَ، وَالْخَـيْرُ كُلُّـهُ بِيَـدَيْـكَ، وَالشَّرُّ لَيْـسَ إِلَـيْكَ، أَنَا بِكَ وَإِلَيْـكَ، تَبَـارَكْتَ وَتَعَـالَيتَ أَسْتَغْـفِرُكَ وَأَتُوبُ إِلَـيْكَ.
Wajjahtu wajhiya lillazee fataras-samawati wal-arda haneefan wama ana minal-mushrikeen, inna salatee wanusukee wamahyaya wamamatee lillahi rabbil-'alameen, la shareeka lahu wabithalika umirtu wa-ana minal-muslimeen. Allahumma antal-maliku la ilaha illa ant. anta rabbee wa-ana 'abduk, zalamtu nafsee wa'taraftu bizanbee faghfir lee thunoobee jamee'an innahu la yaghfiruz-zunooba illa ant.wahdinee li-ahsanil-akhlaki la yahdee li-ahsaniha illa ant, wasrif 'annee sayyi-aha la yasrifu 'annee sayyi-aha illa ant, labbayka wasa'dayk,walkhayru kulluhu biyadayk, washsharru laysa ilayk, ana bika wa-ilayk, tabarakta wata'alayt, astaghfiruka wa-atoobu ilayka.

Na juya fuskata ga wanda ya kagi halittar sammai da kassai, ina mai karkata ga addini na gaskiya, kuma ni ba na cikin mushrikai. Lallai sallata da ayyukan ibadata da rayuwata da mutuwata na Allah ne, Ubangijin talikai; babu abokin tarayya a gare Shi, kuma da wannan aka umarce ni, kuma ni ina daga Cikin Musulmi. Ya Allah! Kai ne Sarki, babu abin bautawa da gaskiya sai Kai; kai ne Ubangijina, kuma ni bawanka ne, na zalunci kaina, kuma na tabbata da zunubina; Ka gafarta mini zunubaina dukkanninsu, ba wanda yake gafarta zunubai sai Kai; Ka gusar da miyagunsu daga gare ni, babu wanda zai gusar da miyagunsu daga gareni sai Kai. Amsa maka, da biyayya gare ka bayan biyayya; kuma arziki naka ne, kuma alherin dukkaninsa yana hannunka, sharri kuma ba a danganta shi gare Ka. Ni kuma dacewata tana gare Ka, kuma gare Ka nake fakewa. Alherinka ya yawaita, kuma Ka daukaka. Ina neman gafarrka, kuma ina tuba gare Ka.


اللّهُـمَّ رَبَّ جِـبْرَائِيلَ، وَمِيكَـائِيلَ، وَإِسْـرَافِيلَ، فَاطِرَ السَّمَوَاتِ وَالأَرْضِ، عَالِمَ الغَيْبِ وَالشَّهَادَةِ أَنْتَ تَحْكُمُ بَيْـنَ عِبَادِكَ فِيمَا كَانُوا فيهِ يَخْتَلِفُونَ. اهْدِنِي لِمَا اخْتُلِفَ فِيهِ مِنَ الْحَقِّ  بِإِذْنِكَ، إِنَّـكَ تَهْـدِي مَنْ تَشَـاءُ إِلَى صِرَاطٍ مُسْتَقَيمٍ.
Allahumma rabba jibra-eel, wameeka-eel, wa-israfeel fatiras-samawati walard, 'alimal-ghaybi washshahadah, anta tahkumu bayna 'ibadika feema kanoo feehi yakhtal


Please to your brothers and sisters 

ADDU'AR TAFIYA DA SHIGA DA FITA DAGA MASALLACI


Addu'ar tafiya Zuwa Masallaci

اللّهُـمَّ اجْعَـلْ فِي قَلْبِـي نُورًا، وَفِي لِسَـانِي نُورًا، فِي سَمْعِي نُورًا، فِي بَصَرِي نُورًا، مِنْ خَلْفِي نُورًا،  وَمِنْ أَمَامِـي نُورًا، وَ مِنْ خَلْفِي نُوراً، فِي نَفْسِي نُوراً، وَأَعْظِمْ لِي نُوراً، وَعَظِّمْ نُوراً، وَاجْعَلْ لِي نُوراً ، وَاجْعَلْنِي نُوراً، اَللُّهُمَّ أَعْطِنِي نُوراً، وَاجْعَلْ فِي عَصَبِي نُوراً، وَفِي لَحْمِي نُوراً، وَفِي دَمِي نُوراً ، وَفِي شَعْرِي نُوراً، وَفِي بَشَرِي نُوراً ". "اَللَّهُمَّ اجْعَلْ لِي نُوراً فِي قَبْرِي .. وَنُوراً فِي عِظَامِي، وَزِدْنِي نُوراً، وَزِدْنِي نُوراً، وَزِدْنِي نُوراً، وَهَبْ لِي نُوراً عَلَى نُوراً.
Allahumma j'al fi kalbi nuran, wa fi lisani nuran, wa fi sam'i nuran, wa fi basari nuran, wa min fawki nuran, wa min tahti nuran, wa 'an yamini nuran, wa 'an shimali nuran, wa min amami nuran, wa min khalfi nuran waj'al fi nafsi nuran, wa a'zim li nuran, wa 'azzim li nuran. Wa j'al li nuran, wa j'alni nuran. Allahumma a'tini nuran, wa j'al fi 'asabi nuran, wa fi lahmi nuran, wa fi dami nuran, wa fi sha'ri nuran, wa fi bashari nuran. (Allahumma j'al lin nuran fi kabri, wa nuran fi izami)
(wa zidni nuran, wa zidni nuran, wa zidni nuran) (wa hab li nuran 'ala nur).

Ya Allah ka sanya haske a cikin zuciyata, da haske a kan harshena, da haske a gabana, da haske a damana, da haske a haguna, da haske a gabana, da haske a bayana; Ka sanya haske a cikin raina, Ka girmama haske gare ni, ka girmama min haske, ka sanya haske gare ni, Ka sanya ni (na zama) haske, Ka sanya haske a cikin jijiyoyina, da haske a cikin namana, da haske a cikin gashina, da haske a cikin fatata, Ya Allah Ka sanya mini haske a cikin kabarina, da haske a cikin kasusuwana, ka kara mini haske, Ka kara mini haske, Ka kara mini haske, Ka ba ni haske a kan haske.


Addu'ar Shiga Masallaci

أَعوذُ باللهِ العَظيـم وَبِوَجْهِـهِ الكَرِيـم وَسُلْطـانِه القَديـم مِنَ الشّيْـطانِ الرَّجـيم،[ بِسْـمِ الله، وَالصَّلاةُ] [وَالسَّلامُ عَلى رَسولِ الله]، اللّهُـمَّ افْتَـحْ لي أَبْوابَ رَحْمَتـِك . 
A'uzu billahil-azeem wabiwajhihil-kareem wasultanihil-kadeem minash-shaytanir-rajeem, 
[bismil-lah, wassalatu] [wassalamu AAala rasoolil-lah] , allahumma iftah lee abwaba rahmatik.

Ina neman tsarin Allah mai girma, da na fuskarsa mai alfarma, da na mulkinsa dadadde, daga shaidan tsinanne. Da sunan Allah, tisara da Aminci su tabbata ga Manzon Allah. Ya Allah! Ka bude mini kofofin rahamarKa.





Addu'ar Fita Daga Masallaci.

بِسمِ الله وَالصّلاةُ وَالسّلامُ عَلى رَسولِ الله، اللّهُـمَّ إِنّـي أَسْأَلُكَ مِـنْ فَضْـلِك، اللّهُـمَّ اعصِمْنـي مِنَ الشَّيْـطانِ الرَّجـيم.

Bismil-lah wassalatu wassalamu ala rasoolil-lah, allahumma innee as-aluka min fadlik, allahumma iAAsimnee minash-shayta
nir-rajeem.

Da sunan Allah tsira da Aminci su tabbata ga Manzon Allah. Ya Allah! Ina rokonka daga falalarka. Ya Allah! Ka kare ni daga shaidan tsinanne.

Please share to your brothers and sisters